Shugaban Hukumar Kwallon Kafa ta kasar Wales Kieran O’Connor ya ce matakin kasar Birtaniya da Jamhuriyar Ireland na daukar nauyin gasar cin kofin duniya ta shekara ta 2030 mataki ne mai matukar muhimmanci.
A shekara ta 2022 ne Ƙasashe za su fara bada takardar bukatarsu ta daukar nauyin gasar, kafin daga bisani a yanke hukunci kan kasar da za a sahale mata.
O’Connor ya bayyana cewa jinkiri da aka samu wajen gudanar da gasar Euro ta 2020 ba zai tala burki wajen ayyana kasar da za ta dauki nauyin gasar cin kofin duniyar ta 2030 ba.
A watan Maris ne dai Firai Ministan Birtaniya Boris Johnson ya sanar da aniyar kasashen Birtaniya da Ireland din na daukar nauyin gasar, inda ya ce yanzu kam lokaci ya yi.
Da yake magana da tashar Labarin Wasanni na BBC, O’Connor ya ce za su zauna da sauran hukumomin kwallon kafa na kasar don samun goyon bayansu.