Majiyoyin tsaro a Nijeriya sun ce sojoji da dama ne suka rasa rayukansu, sakamakon harin kwanton bauna da mayakan Boko Haram suka kai masu kusa da garin Gudumbali da ke jihar Borno a ranar Litinin da ta gabata.
Harin na zuwa ne bayan da sojojin ke kan hanyarsu ta kai dauki ne ga wasu sojojin Najeriya da na Chadi da ke kokarin kwace garin na Gudumbali daga ‘yan Boko Haram, inda mayakan suka yi amfani da mayan makamai ciki har da rokoki a kansu, shaidu sun ce an kashe sojoji gommai tare da lalata motoci da makamansu.
Wannan harin na dada munna ta yada ‘yan Boko Haram ke ci gaba da zama babbar barrazana ga gwamnatin Nijeriya.