Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, a ranar Laraba, ya ce ya damu Matuƙa da kisan wani limamin cocin Katolika, John Cheitnum na Kafanchan Catholic Diocese, kwanaki huɗu bayan da wasu ƴan bindiga sun kama shi.
A cewar wata sanar wa da babban Mai Taimaka masa na Musamman kan harkokin yaɗa labarai, Garba Shehu ya sanya wa hannu, shugaban ya sake tabbatar wa ƴan Najeriya cewa ya Ƙudiri aniyar murƙushe ƴan ta’addan da ya bayyana a matsayin maƙiyan bil’adama.
Sanarwar mai suna ‘Shugaba Buhari ya yi Allah wadai da kisan gillar da aka yi wa limamin Ɗarikar Katolika a Kaduna, ya kuma kira shi a matsayin abin ƙyama da wulakanci.’
KARANTA WANNAN LABARIN: Abba Kyari: Yadda Na Ɓoye Daga Ƴan Ta’addan Da Suka Kai Hari Gidan Yarin Kuje
Jaridar PUNCH ta ruwaito cewa, Cheitnum, wanda aka yi garkuwa da shi tare da wani limamin coci a ranar Juma’a 15 ga watan Yuli, an samu gawarsa kwanaki.
A wata sanarwa da ta fitar a ranar Talata, limamin cocin Katolika Kafanchan ya sanar da cewa an kashe Cheitnum ne a daren da aka sace shi kuma an gano gawarsa da ta riga ta ruɓw a ranar Talata.
Da yake mayar da martani kan lamarin, Buhari ya ce, “Na damu matuƙa da kisan da wasu ƴan ta’adda suka yi wa wannan babban malamin addini, wadanda da alamu sun yi niyyar kawo ruɗani da hargitsi a ƙasar nan.
” Ya bayyana cewa hare-haren da ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutanen da ba su ji ba ba su gani ba, da suka haɗa da masu Addini, wani lamari ne da ke matuƙar damun wannan gwamnati, domin tsaro na ɗaya daga cikin manyan al’amuran da muka alƙawarta a yaƙin neman zaɓe.
“Bari in tabbatarwa ƴan Najeriya cewa Ƙudiri na kan wannan batu ya tabbata kamar yadda aka saba.
A koda yaushe na sanya ya zama wajibi na rika kiran Shugabannin tsaro a kai a kai domin tattauna waɗannan ƙalubale da kuma hanyar da za a bi.
“Ba zan bari shugabannin tsaro su huta ba sai dai kuma har sai mun sami mafita mai inganci kan wannan matsalar tsaro da ke damun mu.
Tsaron dukkan ƴan Nijeriya shi ne babban abin dana sanya a gaba, kuma ina tabbatar wa ƴan Nijeriya cewa mun Ƙudiri aniyar murƙushe Waɗannan maƙiya bil’adama da duk wani abu da muke da shi,” in ji Shugaban.
Ya mika ta’aziyyar sa ga iyalan mamacin da shugabannin Ƙungiyar Kiristoci ta Najeriya a jihar Kaduna bisa rasuwar Cheitnum.