• Shugaban kasa Buhari ya gana da Ibrahim Gambari da Kuma ministan kwadago na kasa.
• Taron na su ya sa, ba kungiyar NLC ba zata goma yajin aiki ba a Kaduna.
• “Na Bai wa Shugaban kasa Buhari shawarar kawar da matsalar tsaro a yankin Kudu maso Gabashin kasar” inji Christ Ngige.
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya gana da Shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa Ibrahim Gambari, ministan kwadago Christ Ngige, domin tauttauna a kan matsalar rashin tsaro a yankin Kudu maso Gabashin kasar nan, da kuma rikicin yan kwadago a jihar Kaduna.
Taron ya gudana ne a fadar shugaban kasa dake Abuja a yau lahadi.
Lokacin da ya ke zantawa da manema Labarai bayan taron, Mr Ngige ya ce, taron ya magance bukatar sake shiga yajin aiki a jihar Kaduna.
Jaridar Premium Times ta ruwaito yadda jagorancin gamayyar kungiyar kwadago ta kasa NLC, ta rubutawa shugaba Buhari yarjejeniyar da gwamnatin jihar Kaduna ta karya, a tsakanin bangarorin biyu, da su ka kulle tun a watan Afurilu da ya gabata.
KARANTA WANNAN LABARIN: Mutane 14 sun mutu a harin yan bindiga a ofishin yan sandan jihar Benue
Idan za a iya tunawa, gwamnatin tarayya, ta bangaren ministan kwadago, ta zauna da bangarorin biyu, domin janye yajin aikinkin gargadi da kungiyar NLC ta shiga a jihar Kaduna.
Mr Ngige ya kuma ce, “Mun duba bangaren gwamnatin jihar Kaduna, da na kungiyar kwadago, inda mukayi kokarin da katar da yajin aikin, kuma muka samar da wani kwamiti dake dauke da mambobi daga bangarorin biyu, don su tauttauna a tsakanin su, domin samun matsaya da kuma dai-dai to” inji shi.
Lokacin da ya ke karin haske, dangane da rikice-rikicen da ake samu a Kudu maso Gabashin kasar nan kuwa, ministan ya ce, ya mika wasu bukatu ga shugaba kasa Buhari, bisa irin yadda mutane ke nuna koken su a kan lamarin.
Comments 1