By Abbas Yakubu Yaura
Shugaban kasa Muhammadu Buhari da yammacin ranar Talata ya isa birnin Paris na kasar Faransa domin ziyarar aiki ta yini daya a matsayin bakon shugaba Emmanuel Macron a Palais de l’Élysée.
Mai magana da yawun shugaban kasa, Femi Adesina, a wata sanarwa daya fitar, yace Buhari dai zai halarci taron zaman lafiya na Paris na kwanaki uku (PPF), daga ranar 11 zuwa 13 ga watan Nuwamba.
Yace yayin ziyarar aiki a ranar Laraba, Buhari zai gana da takwaransa na Faransa don tattaunawa kan batutuwan da suka shafi kasashen biyu, musamman kan karfafa dangantakar tattalin arziki, inganta hadin gwiwa a fannin tsaro, da yin aiki tare a fannin ilimi, lafiya da kuma dakile barazanar cutar COVID-19. ga tattalin arzikin duniya.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa Adesina yace daga ranar Alhamis, Buhari zai hadu da shugabannin duniya, shugabannin kungiyoyin kasa da kasa, shugabannin kungiyoyin farar hula da kuma kamfanoni masu zaman kansu a Grande Halle de La Villette, don tsara dabarun gudanar da shugabanci na gari don samar da zaman lafiya, tare da taro, manyan darajoji da kuma taron karawa juna sani.
Sannan yace, an shirya shugaban kasar zai yi jawabi a wajen taron domin bayyana irin abubuwan da Najeriya ke fama da shi ga duniya, da kuma kokarin da ake yi na kawo zaman lafiya.
Sauran wadanda suka yi jawabi, a cewarsa, sun hada da shugaba Macron, mataimakin shugaban kasar Kamala Harris na Amurka, da Sheikh Hasina, firaministan kasar Bangladesh.
Adesina yace a wannan shekara, shugabannin za su yi nazari kan ayyuka 80 da aka tsara don inganta zaman lafiya a fadin duniya da kuma tabbatar da zaman lafiya mai kyau kamar sake fasalin tsarin jari hujja don karin tasiri ga tattalin arzikin duniya, da mayar da martani ga gaggawar sauyin yanayi, labaran karya da kalubalen dake tattare da shi, aikin jarida da tsaro na yanar gizo.