Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya kafa sabon kwamitin da zasu taimakawa gwamnatinsa wajen inganta wutar lantarki a faɗin ƙasar nan.
Daga cikin wanda Buhari ya zaba a matsayin ‘yan kwamitin sun haɗa da Antoni Janar kuma Ministan Shari’a na ƙasa Abubakar Malami SAN, Ministan Wuta Saleh Mamman, Ministan ayyuka da gidaje Babatunde Fashola da kuma Ministar harkokin kuɗaɗe Misis Zainab Ahmed.
Sanarwar ta ce “Harkar wuta tana ɗaya daga cikin abubuwan ci gaban rayuwa, kuma na ɗaya daga cikin abinda wannan gwamnati tasa gaba”, cewar Shugaba Buhari.
Buhari ya ƙara da cewa shi yasa gwamantinsa ta ƙirƙiro wannan kwamitin domin tabbatar da cewa ‘yan Najeriya sun samu ingantacciyar wuta.