Fitaccen dan siyasar nan na Nijeriya, Buba Galadima, ya bayyana cewa shugaba Buhari ya kasa cirewa Talaka kitse a wuta. Buba Galadima ya bayyana hakan ne a yayin hirar da da ya yi da gidan rediyo da Talabijin na MADUBI a ranar Larabar 19 ga watan Agustan 2020 a cikin shirin MENE NE MAKOMAR NIJERIYA BAYAN MULKIN JANAR BUHARI?
Buba Galadima ya bayyana cewa; “na bata akasarin rayuwata na shekara goma sha biyar, ina bautawa tafiyar Janaral Muhammadu Buhari, da zaton cewa zai iya maganin abubuwa da yawan gaske da suka addabi kasarnan. Zai iya kuma daukowa Talaka kitse a wuta.”
Ya ci gaba da cewa; “da kuma karin cewa irin tashin-tashina da kuma rashin zaman lafiya da ake da shi a kasarnan, a matsayinsa na wanda ya taba zama shugaban Nijeriya. A matsayinsa na wanda ya taba zama kwamandan soja, a matsayinsa na wanda ya taba zama GOC, wato zai iya magance wadannan annoba da tashin-tashina a kasarnan, to ga shi ba haka aka so ba, kanin miji ya fi miji kyau”.
Ya karkare da cewa; “sai muka tarar cewa ashe ma gwara mutumin da bai taba rike mukamin siyasa ba, a iya cewa ma, duk wani dan Nijeriya ya yadda cewa jiya ma ta fi yau.” Ya tabbatar.