Shugaba Muhammad Buhari ya sauka a garin Abeokuta na jihar Ogun. Buhari ya kai ziyara garin ne domin ayyukan da gwamna mai barin gado, Sanata Ibikunle Amosun, yayi.
Shugaban ya sauke garin ne da misalin karfe 10:18am, a jirgin shelikwafta mai lamba NAF 540, a filin Arcade dake sakatariyar jihar.
Ya samu tarba daga gwamnan jihar, Ibikunle Amosun, Gwamnan jihar Legas, Akinwunmi Ambode, gwamnan jihar Ekiti, Kayode Feyemi da gwamnan jihar Ondo, Rotimi Akeredolu.
Ministan lafiya, Prof Isaac Adewole; Sarkin Oba Adedotun Gbadebo da tsohon mai bada shawara a jami’iyyar APC, Muiz Banire.
Daily Trust ta rawaito cewa Buhari yaki zuwa wajen bude ganuwar gari, inda ya tafi wajen manyan ‘yan siyasa da hukumomin tsaron jihar domin tattauna batutuwan da suke akwai na matsalar tsaro.