Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya mika sakon gaisuwa ga sakataren gwamnatin tarayya (SGF), Boss Gidahyelda Mustapha na murnar cikar sa shekaru 66 a duniya.
KARANTA WANNAN LABARIN: Amurka Ta Yabawa Najeriya Kan Kokarin Tabbatar Da Tsarin Dimokuraɗiyya
Shugaban, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar ta hannun mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Malam Garba Shehu, ya yabawa Mustapha bisa sadaukarwar da ya yi wajen gina kasa tun yana matashi a shekarunsa 80, inda ya ce ya tsaya tsayin daka a harkokin shari’a, siyasa da shugabanci, tare da yin ayyuka masu banbance-banbance a cikin al’umma.
Shugaba Buhari ya jinjinawa kudurinsa na tabbatar da dorewar ra’ayoyi, aiki tare, daidaito da kuma ingantacciyar hanyar sauya manufofi zuwa ga riba ga ‘yan Najeriya.
Ya ce matsayin jagora mai tarihi na jagoran siyasa kuma ƙwararren ma’aikacin gwamnati, kamar shugabantar Kwamitin Task Force na Shugaban Ƙasa kan cutar Covid-19, zai ci gaba da ba shi fifiko don karrama shi.
Shugaban ya bi sahun ‘yan uwa da abokan arziki da ‘yan siyasa musamman ‘ya’yan jam’iyyar APC wajen biki tare da jiga-jigan shari’a kuma tsohon Manajan Darakta na Hukumar Kula da Ruwa ta Najeriya (NIWA).
Shugaba Buhari ya kuma yi addu’ar Allah ya karawa Mustapha da iyalansa nisan kwana mai amfani.
A wani labarin kuma, Gwamnatin Legas Ta Bada Umurnin Komawa Makarantu Ranar Litinin
Gwamnatin jihar Legas ta umarci dukkan makarantu da su fara zagon karatun shekarar 2022/2023 a ranar 5 ga watan Satumbar 2022.
Bayanan hakan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da babban daraktan ofishin tabbatar da ingancin ilimi na jihar, Abiola Seriki-Ayeni, ya fitar a ranar Asabar.