Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bada umarnin yin bincike tare da gano abinda ya faru a tsakanin wasu jami’an tsaron dake fadar gwamnatin tarayya wanda ya kai ga yin harbe-harbe.
Wannan ya fito ne dauke cikin wata sanarwa da Malam Garba Shehu mai magana da yawun shugaban kasa ya fitar a jiya Lahadi.
Shehu yace shugaban kasa ya bada urmanin ne domin yin bincike da gano abinda ya faru tsakanin mai dakin shugaban kasa Aisha Buhari, da kuma wani jami’in shugaban kasa mai suna Sabiu Yusif, a karshen makon daya gabata.
https://dimokuradiyya.com.ng/za-a-hukunta-masu-cin-zarafin-mata-shugaba-buhari/
Lamarin dai ya faru ne bayan da Yusuf ya dawo daga ziyarar iyalinsa daga jihar Legas, Wanda wasu suke ganin ya kamata ya killace kansa saboda yanayin da ake ciki na annobar sarke numfashi. Hakan ne ya kawo rashin fahimta tsakaninsa da mai dakin shugaban kasa har ya kai ga wasu jami’an tsaronta sun yi harbe-harbe, Wanda ba a san dalilin yin hakan ba.
Ya zuwa yanzu dai za a gudanar da bincike don gano bakin zaren, duk da cewa akwai rade-radin da ake na cewa Aisha bata shiru da Yusuf din Wanda yake akwai alaka mai karfi tsakaninsa da shugaba Muhammadu Buhari.