Buhari zai murƙushe Ƴan Ta’adda kafin 2023 – Femi Adesina
A ranar Larabar da ta gabata ne mai baiwa shugaban kasa Muhammadu Buhari shawara kan harkokin yada labarai Femi Adesina ya bayyana cewa shugaban nasa zai kawo karshen duk wani kalubale na rashin tsaro kafin mika mulki ga wanda zai gaje shi a shekarar 2023.
Adesina ya ce za a dakatar da sace-sacen mutane da ‘yan fashi da makami kafin zabe mai zuwa.
KARANTA WANNAN LABARIN: Zaben 2023: Bola Tinubu ya yi nasara a Kotu
Ya yi magana ne a Abuja ranar Laraba a taron shekara-shekara kan tsaro da sadarwa.
Mai magana da yawun shugaban kasar wanda ya jagoranci taron ya bayyana cewa alkalumma a fadin kasar sun tabbatar da cewa sannu a hankali kasar na shawo kan kalubalen rashin tsaro da Buhari ya gada.
Adesina ya yi tsokaci kan wasu sassan kasar da ke fama da rikici inda ya kara da cewa lamarin ya lafa cikin ‘yan watannin da suka gabata.
“Ko da yake wasu, saboda dalilan da aka fi sani da su, ba za su yarda ba, amma gaskiya da gaskiya ita ce Najeriya na shawo kan kalubalen rashin tsaro.
“Al’amarin ya lafa, kuma shugaban kasa Muhammadu Buhari zai bar kasar fiye da yadda ya gada.
“Tsaro na kara samun sauki kullum kuma shugaba Buhari zai yi nasara a yakin kafin ya mika mulki a shekara mai zuwa,” in ji shi
A wani labarin kuma: Na yarda Afenifere, Adebanjo suna magana kan Adalci – Peter Obi
Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, Peter Obi, ya ce abin da kungiyar Afenifere, babbar kungiyar al’adun kabilar Yarbawa, ke tsayawa a kai a yau shi ne makomar Najeriya.
Obi ya bayyana hakan ne a ranar Larabar da ta gabata yayin gangamin yakin neman zaben shugaban kasa a Ibadan, babban birnin jihar Oyo.