Shugaban kasa Muhammadu Buhari a jawabin da ya yiwa ‘yan kasa a cikin daren yau Litinin, ya ce daga ranar 4 ga watan Mayun nan za a fara cire dokar takaita zirga-zirgar da aka sanya a Legas da Abuja da kuma Ogun.
Buhari bayan sassauta dokar hana zirga-zirgar ta tsawon sa’o’i 24 a jihohin 3 din, amma ya sanya dokar hana fitar dare wacce za ta soma aiki daga karfe 8 na dare zuwa 6 na safe, haka zalika ya zama tilas mutane su rika sanya takunkumin fuska da hanci a duk lokacin da za su fita daga gidajensu.
Buhari ya ce za a sassauta dokar hana zirga-zirgar ce bayan tabbatar da cewa an karfafa shirin yi wa mutane akalla dubu 2 a fadin kasar gwajin cutar Korona a rana guda.