An Sami tirka tirka lokacin da kungiyar malaman jami’o’i (ASUU) ta ki amincewa da sa hannun gidan rediyon Berekete Family na kawo karshen yajin aikin da ake yi.
Kungiyar ASUU dai ta shiga yajin aikin ne tun watan Fabrairu kuma duk kokarin da malaman suka yi na komawa ajujuwa bai haifar da da mai ido ba.
A safiyar ranar Asabar ne jagoran shirin na rediyo, Ahmad Isah, wanda aka fi sani da Ordinary President, ya gayyaci shugaban ASUU, Farfesa Emmanuel Osodeke, da tawagarsa, domin bayyana wa ‘yan Nijeriya matsalolin da suka dade suna fama da su, tare da bayyana dalilin da yasa har yanzu kungiyar ke yajin aiki.
Isah ya kuma ce ya kafa asusun ajiyar banki na musamman da ke zama a bankin TAJ domin tara wa kungiyar kudade, da nufin kawo karshen yajin aikin.
Bisa dukkan alamu dai don shawo kan ASUU ta sayi tunanin shiga tsakani, Isah ya fito fili ya nuna tsabar kudi naira miliyan 50 da gwamna Udom Emmanuel na jihar Akwa Ibom ya bayar a matsayin tallafinsa.
Nan take aka baje kolin kudin, Shugaban ASUU ya fusata da wannan lamari, yana mai cewa bai kamata a danganta su da irin wannan ba.
A lokacin ne Isah ya yi barazanar dakatar da shiga tsakani kuma da yawa daga cikin ‘yan Najeriya da suka buga waya a lokacin shirin sun bayyana ASUU a matsayin “marasa hankali”.
Bukatun malaman da suka fi daukar hankali sun hada da, bayar da kudade na farfado da jami’o’in gwamnati, Lamunin na fannin Ilimi, Maganganun Fassara na Jami’a (UTAS) da basussukan da suke bi.
Sauran sun hada da sake tattaunawa na 2009 ASUU da gwamnatin Tarayya kan Yarjejeniyar da kuma rashin daidaito a Tsarin Bayanan Biyan Kuɗi na Ma’aikata.
A wata hira da aka yi da shi a watan da ya gabata, Osedeke ya shaida wa NAN cewa babu daya daga cikin wadannan bukatu da gwamnatin tarayya ta cika.