By Abbas Yakubu Yaura
Shugaban kasar Kenya Uhuru Kenyatta ya yi kira ga shugabannin kasashe masu karfin tattalin arziki da su yi la’akari da “bukatu na musamman da yanayin Afirka.”a yakin da ake da sauyin yanayi.
Da yake jawabi ga duniya a taron sauyin yanayi na COP26 a Glasgow, yace Kenya ta ɓullo da wani shiri na kiyaye ƙarancin yanayin haɓakar carbon nan da shekarar 2030.
Ya kuma yi kira ga shugabannin kasashen da suka ci gaba da su ba da tallafi ga Afirka saboda Afirka na da nata kalubale.
Dubban kananan jahohin tsibirai da kuma manyan garuruwan dake kwance a duniya na fargabar tasirin sauyin yanayi zai iya haifar wa kasarsu matsala idan ba a dauki matakan gaggawa ba.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa Shugaban Seychelles, Wavel John Charles Ramkalawan yace “Lokacin dana ji maganar tana tashi a teku, ina jin tsoro saboda yana kawo fahimtar cewa tsibiran kasata za su rasa dukkan ayyukan tattalin arziki dake faruwa a gabar teku,” in ji shi yayin jawabinsa.
Ramkalawan ya kara da cewa yana tsoron Seychelles, “kyakkyawan tsibiran guda dari 115,” na iya raguwa zuwa kasa da tsibiran 50 yayin da murjani reefs suka bace.sannan yace Seychelles “ba ta da alhaki” ga halakar duniya, “amma akasin haka muna yin iyakar kokarinmu.”
Wasu gungun masu fafutukar ganin sauyin yanayi sun hallara a wajen taron, inda suka yi zanga-zangar nuna adawa da amfani da makamashin mai. Suka aika da sako cewa MUNA KALLON KA