Jigo a jam’iyyar APC dake jihar Ondo, Morayo Lebi a ranar Juma’a ya rabawa mutane 120 naira dubu biyar-biyar wadanda suka fito daga yankin Kudancin Ondo a wani mataki na tallafa musu a daidia wannan lokaci da gwamnati ke killace al’umma a ci gaba domin dakile yaduwar cutar Coronavirus.
Lebi, wanda yake yana neman takarar Sanata ne a yankin, ya ce ya bada wannan tallafin ne domin saukaka radadin talauci bisa yadda aka killace al’umma a gida saboda annobar COVID-19.
Ya kuma tabbatar da cewa har wala yau zai tallafawa zaurawa da kuma marayu domin suma sun amfana daga wannan tallafin na shi.