Gwamnan Jihar Jigawa Alhaji Badaru Abubakar ya sanar da buɗe iyakokin jihar da sauran jihohi, wanda aka rufe tun a watan Maris saboda annobar cutar korona.
Gwamnan wanda ya bayyana haka a taron manema labarai ranar Asabar a Dutse babban birnin jihar, ya ce za a buɗe zirga-zirga tsakanin jihar da sauran jihohi cikin tsauraran matakan kariya daga cutar kamar yadda cibiyar dakile cututtuka masu yaduwa ta NCDC ta tanadar.
Kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN ya rawaito cewa buɗewar tana zuwa ne mako guda bayan an buɗe kasuwannin jihar da ke ci sati-sati.
Tuni aka sallami mutum 307 daga cikin 317 da suka kamu da cutar bayan sun warke, yayin da da guda 9 suka riga mu gidan gaskiya.
https://dimokuradiyya.com.ng/za-a-hadawa-almajirai-da-karatun-boko-a-jigawa/
“Muna ta addu’ar kada mu koma cikin irin wancan lokacin domin al’umma sun wahala ba kadan ba,” in ji gwamnan.
“Yanzu haka mutum ɗaya ne mai ɗauke da cutar yake jinya, inda sauran da ke cibiyar killace mutane suka warke kuma an sallame su.
Kamfanin dillancin labarai na ƙasa, ya ce gwamnan ya bayyana cewa Gwamnatin tarayya ta bai wa jihar tallafin naira biliyan ɗaya, ƙari a kan mota 150 cike da hatsi domin raba wa marasa ƙarfi.
Gwamnan ya kara da cewa, a halin yanzu ba zasu bude makarantu ba har sai hukuncin da masana suka yanke sannan zasu ga abinda ya dace.