Kwanaki biyu da sallamar ragowar mutane biyar daga cibiyar killace masu cutar sarke numfashi a jihar Sokoto, an sake samun mutane 11 dauke da cutar.
Wannan ya fito ne daga jawabin da kwamitin kar ta kwana kan cutar na jihar ta fitar cewa karin wanda aka samu masu dauke da cutar na daga cikin Almajiran da aka kawo ne daga jihar Kaduna.
Almajiran an dawo da su daga Zaria dake jihar Kaduna a ranar 4 ga watan Yulin da muke ciki, “dukkanin Almajiran su 33 an killace a cibiyar killace masu dauke da cutar dake wajen daukar horon masu yiwa kasa hidima dake Wamakko”.
“A lokacin da suka iso an musu gwaji, kuma an rashin nasara inda aka samu 11 daga cikinsu na dauke da cutar”.
https://dimokuradiyya.com.ng/a-karon-farko-coronavirus-ta-bulla-a-sokoto/
A cikin jawabin an bayyana cewa Almajiran basu yi wata mu’amala da iyayensu ba.
Gwamnatin Sokoto tace zata yi hadin guiwa da gwamnatin Kaduna domin yin binciken wanda Almajiran suka yi hulda dasu.
Idan ba a manta ba cikin satin da ya gabata ne gwamnatin jihar ta sallami masu jinyar Corona dake jihar su 101 daga cibiyoyin killace kai.
Dakta Ali Inname wamda shi ne shugaban kwamitin kar ta kwana na jihar ya bayyana cewa a ranar Juma’ar data gabata jihar baya da saurin wanda yake dauke da cutar.