Tun da cutar Corona ta bulla a watan Fabrairun shekarar nan, manyan makarantu da kanana kama tun daga Jami’o’i, Kwaleji da kuma mankarantun Firamare da Sakandire gwamnatin tarayya ta bada umarnin kulle su saboda ba lallai bangaren ilimi ya iya bin dokokin da aka shimfida wajen ganin an yaki cutar ta sarke numfashi ba.
Tun da ya kasance cutar tana kan ganiyarta, a yanzu a iya cewa ba lallai bane a bude makarantu ba, saboda hakan na iya jefa rayuwa yara manyan gobe cikin wani mayucin hali.
Misali a kasar Korea ta Kudu gwamnati ta bada damar bude makarantu domin ci gaba da karatu amma daga baya ta sake sawa a kulle biyo bayan samun yara da dama da kamuwa da cutar ta COVID19, hakan yasa a Najeriya ba lallai a samu damar bude makarantu yanzu ba sai dai zuwa gaba idan an ga abinda hali ya yi.
https://dimokuradiyya.com.ng/gwamnati-ta-bada-sharadi-kafin-bude-makarantu-masallatai-coci-da-sauran-harkokin-yau-da-kullum/
Sai dai wasu kasashe sun rungumi tsarin koyarwa ta hanyar Yanar-Gizo, amma a nan kasar ba lallai wannan hanya ta yi tasiri ba, duba da irin daliban da muke da su wanda da yawansu basu waye da tsarin ba. Uwa-uba kuwa, su kansu malaman da yawansu basu iya sarrafa na’ura mai kwakwalwa ba face kuma su koyar ta wannan sabon tsari.
Dawowar makarantu domin ci gaba da daukar karatu, a iya cewa sai baba gani, duba da irin yadda kasar ta cintsi kai da kuma irin rawar da gwamnati ka iya takawa wajen bude makarantun.