A cigaba da kwaso ‘yan Najeriya daga kasashen ketare wanda dokar kulle ta ritsa dasu, Najeriya ta kwaso mutane 292 daga kasar Saudi Arabia zuwa babban birnin tarayya kamar yadda Jaridar Punch ta rawaito.
A yammacin ranar Talata ne mutanen suka iso filin tashi da sauka na Nnamdi Azikwe daga birnin tarayya, Abuja.
Ministan harkokin kasashen waje Geoffrey Onyeama ne, ya bayyana hakan a shafinsa na Twitter.
Ya ce mutanen da suka iso yawancinsu mata ne da kuma kananan yara, kuma za a killace su a otal na tsawon mako biyu kamar yadda doka ta tanada, karkashin kulawar hukumar dakile cututtuka ta kasa (NCDC).
“Hukumar Saudi Arabia ta dawo mana da mutane 292, kuma sun iso gida Najeria, a yanzu haka za a killace su ja tsawon mako biyu, karkashin kulawar hukumar dakile cututtuka ta kasa (NCDC)”.
Ya kara da cewa ‘Yan Najeriya da suke kasar Faransa zasu iya tasowa zuwa Cotonou wanda daga nan ne za a yi shirin kwaso su zuwa Najeriya.
Ya bayyana hakan ne a yayin da kwamitin kar ta kwana kan cutar COVID19 ke bada karin haske jiya a Abuja.
Onyeama, ya ce gwamnati zata cigaba da kwaso mutanenta dake kasashen ketare ta hanyar amfani da abinda yake hannunta.
Daga: Abubakar Muhammad Usman