By Abbas Yakubu Yaura
Akalla ma’aikatan lafiya takwas ne suka kamu da cutar bayan barkewar cutar zazzabin Lassa a Najeriya.
Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da cibiyar dakile yaduwar cututtuka ta Najeriya ta bayyana cewa adadin wadanda suka mutu sanadiyar cutar ya kai 83.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa a ranar Asabar cutar zazzabin Lassa, cuta ce dake yaduwa a Najeriya a duk shekara amma ana samun karuwar masu kamuwa da cutar a lokacin noman rani.
Hukumar NCDC a shafinta na yanar gizo ta yi kira ga ma’aikatan kiwon lafiya dasu “ci gaba da kasancewa da yawan zargin cutar zazzabin Lassa, su yi taka tsantsan da kuma lura da alamun zazzabin Lassa. Ba duk zazzaɓi ba ne zazzabin cizon sauro”, in ji cibiyar kula da cutar.
A cikin rahoton halin da ake ciki na mako-mako, cibiyar ta lura cewa jimillar ma’aikata takwas ne suka kamu da cutar yayin da adadin wadanda suka mutu ya zuwa yanzu ya kai 83.
Cibiyar ta kara da cewa an samu rahoton bullar cutar guda 4,083 da ake zargi da aikatawa a dukkan jahohin kasar 36 da FCT. “A cikin dukkan wadanda aka tabbatar sun kamu da cutar, an samu kashi 84 cikin 100 a jihohin Edo, Ondo da Taraba,” in ji shi.
NCDC ta kuma kara da cewa, a shekarar 2019, an samu jimillar mutane 796 da suka kamu da cutar, yayin data kuma ta kara dawowa 1,165 da aka tabbatar a shekarar 2020 yayin da annobar cutar ta fi kamari.
Sai dai Darakta Janar na Hukumar NCDC, Dokta Ifedayo Adetifa, ya bayyana cewa NCDC ta aike da wasikun fadakarwa ga jihohi domin sanar dasu halin da ake ciki.