Da Ɗuminsa: Na magance yajin aikin ASUU a rana daya – Jonathan
Tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya bayyana yadda gwamnatinsa ta warware yajin aikin da kungiyar malaman jami’o’i (ASUU) ta yi na tsawon watanni hudu a rana daya.
KARANTA WANNAN LABARIN: Hukumar NSCDC ta kama Masu Gadi 13 a Anambra
Ya bayyana haka ne a ranar Laraba a Abuja, a wajen bikin cika shekaru 70 na Mathew Hassan Kukah, Bishop na darikar Katolika na Sokoto, wanda cibiyar Kukah ta shirya.
Daily Trust ta ruwaito cewa malaman jami’o’in sun shiga yajin aikin ne tun a watan Fabrairu saboda rashin jituwa da gwamnatin tarayya.
“Al’ummar da muke tafiyar da su na da sarkakiya, yanzu maganar yajin aikin ASUU muke yi, a lokacina ASUU ta yi yajin aikin na tsawon watanni hudu, kwamitoci daban-daban suna taruwa suna taro babu abin da ke aiki. Na ce ta yaya yaranmu za su daina zuwa makaranta har tsawon wata hudu? Don haka sai na kira taro na dukkan shugabannin kungiyar ASUU.
“Na jagoranci taron da mataimakina shugaban kasa, babban lauyan gwamnati na can, na ce a daren nan dole ne mu magance matsalar. Babban Lauyan gwamnati yana nan, na biyu na gwamnatin tarayya, ministocin ilimi suna nan, ministocin kwadago akwai ministocin kudi, duk wanda ke da alaka da shi.
“Kuma na yi tunanin cewa kasancewata a wurin zai taimaka mana mu yi abubuwa da sauri. Amma mun kwana, kafin mu gama da misalin karfe 5:30 na safe kafin mu kammala janye yajin aikin, don haka akwai batutuwa,” inji Jonathan.
Ya kara da cewa Bishop Kukah duk da abokantakarsa da shugabanni ya kuma yi musu kaca-kaca a lokacin da ya ji ba su yi wasu abubuwa ba, ciki har da shi kansa.