Da Ɗumi-Ɗumi: JAMB ta amince da Makin Jami’o’i, Kwalejin Kimiyya don guraben Karatu
Hukumar Shirya Jarabawar Share Fagen Shiga Jami’a a ranar Alhamis ta amince da makin da za’a yi amfani dashi a Jami’o’i da Kwalejojin Kimiyya da Fasaha a Ƙasar.
An dauki matakin ne bayan wani zazzafar zama da ya kunshi jami’an JAMB, ma’aikatar ilimi, hukumar kula da jami’o’i ta kasa, da hukumar kula da ilimin fasaha ta kasa da dai sauransu.
KARANTA WANNAN LABARIN: 2022 UTME: Ɗalibai 378,639 ne kawai suka samu maki sama da 200 – JAMB
Ga kwalejin kimiyya da fasaha, an amince da maki 120, yayin da maki 140 aka amince da su a shiga jami’o’i.
A baya dai PUNCH ta ruwaito cewa magatakardan JAMB, Farfesa Ishaq Oloyede, a taron tsare-tsare na 2022 ya bayyana cewa 378,639 ne kawai daga cikin Ɗalibai 1,761,338 da suka rubuta jarabawar ta 2022 suka samu Maki sama da 200 da abinda yayi sama.
Yayin da yake ba da ƙarin kididdiga na jarrabawar 2022, Oloyede ya lura cewa 378,639 sun sami maki sama da 200; Ɗalibai 520,596 ne suka samu maki 190 zuwa sama; 704,991 sun samu maki 180 da sama; 934,103 suma suna da maki 170 da sama; 1,192,057 suka samu maki 160 da sama.
Da yake ƙarin haske, Oloyede ya lura cewa hukumar ta ba wa Ɗalibai masu jiran sakamako yin rajistar UTME na 2022.
“JAMB ta ba da damar masu jiran sakamako su yi rajista da zama na UTME na 2022. Ba za a iya la’akari da waɗannan ‘yan takarar don shiga kan matsayin sakamako ba. Dole ne su gabatar da sakamakon O’level a tashar tashar hukumar kafin fara shiga