Tsohon Shugan kasa, Goodluck Jonathan, ya danganta nasarorin da ya samu a gwamnatin sa ne da addu’o’in da ya yi ta yi. Da yake magana a ranar Juma’a a taron addu’a na uku karo na goma a Cocin, Synod of the Church of Nigeria, Anglican Communion, wanda aka yi a Abuja, Jonathan, ya nemi ‘yan Nijeriya da su ci gaba da yi wa kasar nan addu’a da bayar da goyon bayansu ga kokarin da gwamnatin tarayya ke yi na yaki da rashin tsaro. “A matsayinmu na kasa, tun can farko, mun fuskanci kalubale masu yawa, na batun satar mutane da fashi da makami,” in ji shi. “Hatta yin tafiya zuwa garuruwa na kusa kamar Kaduna, ya zama sai dai a mafarki ga ‘yan Nijeriya. Amma tare da tsananta addu’a kasar nan za ta ga bayan duk wadannan kalubalen. Jonathan kuma ya musanta zargin da ake yi masa na kwashe bilyoyin Naira daga asusun tarayya daga bankuna a lokacin da yake kan mulki. Ya bayyana hakan da cewa, duk karya ce tsadwaronta. Nicholas Okoh, shugaban Cocin na, Church of Nigeria (Anglican Communion), ya koka kan gazawar da shugabanni suka yi na hukunta masu aikata laifi da suke a karkashin su. Ya ce, a halin yanzun kasar nan tana fama da karancin ‘yan siyasan da za su yi wa jama’a aiki. Ya kuma yi nuni ga irin halayan shugabannin da za su yi wa al’umma aiki a kowane mataki a kan gaskiya da adalci. “Mulki yana nufin taimakawa al’umma ne, amma ba shi ne karshen komai ba. Wani mataki ne kadai na yin gwaji a kan inganta taimako ga mutane. “Ya zama tilas mu yi addu’a ga ‘yan siyasan da suke yi wa mutane hidima a mataki na tarayya, Jiha da kananan hukumomi, har ma da Sarakunan gargajiya. “Wasu ‘yan siyasan suna kokarin su nunawa mutane su masu wayo ne ta hanyar sace dukiyarsu su yi ta tara dukiyoyi, ba tare da sun inganta rayuwar al’ummarsu ba. Wannan ne kuma ya sanya muke cikin tsananin karancin shugabannin siyasa maza da mata masu yi wa al’umma aiki.