By Abbas Yakubu Yaura
Wasu mutane uku da ake zargin masu garkuwa da mutane ne a jihar Taraba sun rasa rayukansu a wani fadan daya afku a tsakanin su akan rabon kudin fansa.
Lamarin dai a cewar majiyoyi, ya faru ne kwanaki kadan bayan an biya kudin fansar wani dan kasuwa mazaunin Jalingo da kuma wata matar aure da aka sace makonnin da suka gabata. majiya ta shaida wa manema labarai cewa fadan ya faru ne a gindin wani dutse dake karamar hukumar Ardo Kola a jihar.
Majiyar ta ce mazauna kauyen dake kusa da dutsen sun ji muryoyin dake fitowa daga wajen dutsen, wanda masu garkuwa da mutanen ke iko da shi.
Sannan ya ce an gano gawarwaki uku a wurare daban-daban a kusa da dutsen.
“Masu garkuwa da mutane sun gwabza a tsakaninsu, wasu kuma sun mutu a fadan.Hakan ya faru ne a lokacin rabon kudin fansa amma wannan shi ne karon farko da aka ga gawarwaki,” inji majiyar.
Masu garkuwa da mutane na amfani da Kogin Mallam Garba da ke Jalingo a matsayin hanyar zuwa kogon da suke buya a tsaunin Kwando.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa An gargadi mazauna kauyukan dake kusa da yankin da kada su bayyana wa jami’an tsaro ayyukansu.
Sai dai bayan da aka tuntubi kakakin rundunar ‘yan sandan Taraba, DSP Usman Abdullahi, ya ce rundunar ba ta samu rahoton faruwar lamarin a hukumance ba.
“Yanzu na fita daga Jalingo.idan na gano abinda ke faruwa zan sanar da ku. Duk da haka, idan gaskiya ne cewa masu garkuwa da mutane sun kashe kansu, abin ci gaba ne mai kyau,” in ji PPRO.