Toh rahotannin dake shigomana yanzu yanzu ya nuna cewa adadin wadanda suka mutu sanadiyar girgizan kasar a Afghanistan ya kai mutum 1,000, kamar yadda jami’an gwamnatin Taliban suka bayhanawa kafar yada labarai ta BBC
.
Shugaban Gwamnatin Taliban Hibatullah Akhundzada ya bayyana cewa, daruruwar gidaje sun lalace yayin da adadin wadanda shuka mutu ke cigaba karuwa
Wannan dai shine karo iftila’in girgizar kasar itace dai mafi girma da kasar ta fuskata cikin sama da shekaru 20 da suka gabata.
.
Kana kakakin lardin Paktika Mohammad Amin Hafizi ya bayyanawa kafafen yada labarai cewa, kawo yanzu mutane dubu guda ne suka mutu, yayin da sana da dubu daya da dari biyar suka jikkata.
A wnai labarin kuma na daban.
Da Dumi-Dumi: Shugaba Buhari na ganawa da mambobin majalissar Zartaswa kafin ya shilla Rwanda
Shugaban kasa, Muhammadu Buhari yana jagorantar taron majalisar zartarwa ta tarayya na wannan mako da ke gudana a fadarsa dake Abuja.
Wadanda suka halarci taron sun hada da mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo; Shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Farfesa Ibrahim Gambari; Sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha; Ministocin masana’antu, kasuwanci da zuba jari, Niyi Adebayo; Ayyuka da Gidaje, Babatunde Fashola; Mai shari’a kuma babban lauyan tarayya, Abubakar Malami.
Sauran sun hada da ministar kudi, Dr Zainab Ahmed; Ministan Muhalli, Mohammed Abdullahi; Ministan Babban Birnin Tarayya, Mohammed Bello; karamin mai kula da masana’antu, kasuwanci da zuba jari, Mariam Katagum, karamin ministan muhalli, Sharon Ikeazor, da dai sauransu.
Bayan taron da yammacin ranar Laraba, shugaban zai tashi daga Abuja zuwa Kigali na kasar Ruwanda, domin halartar taron kungiyar kasashen renon Ingila karo na 26, wanda zai gudana daga ranar 20 zuwa 26 ga watan Yuni, 2022.