Daga: Ibrahim Hassan Hausawa
Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama ta Najeriya (NCAA) ta sanar da dakatar da lasisin zirga-zirgar jiragen sama na Dana Airlines (ATL) da kuma takardar shaidar kamfanin Air Operator (AOC) har zuwa wani lokaci, daga tsakar daren Laraba, 20 ga watan Yuli, 2022.
A cewar hukumar, dakatarwar ta biyo bayan sashe na 35 (2) da 3(b) da (4) na dokar zirga-zirgar jiragen sama na shekarar 2006 da kuma sashi na 1.3.3.3 (a) (1) na dokokin zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya CARs shekarar 2015.
KARANTA WANNAN LABARIN: https://dimokuradiyya.com.ng/an-rufe-jamiar-jihar-cross-river-kan-garkuwa-da-%c9%97aliban-ta/
Tun daga lokacin ne aka sanar da dakatarwar da Darakta Janar, Kyaftin Musa Nuhu ya bayar ga mahukuntan kamfanin na jiragen na Dana.
Ya ci gaba da cewa, “Wannan shawarar ta biyo bayan wani bincike na kudi da tattalin arziki da hukumar ta gudanar a kan harkokin sufurin jiragen sama, da kuma sakamakon binciken da aka gudanar a kan harkokin sufurin jiragen sama na kwanan nan, wanda ya nuna cewa kamfanin na Dana ba ya cikin wani hali na matsayi don cika wajiban kuɗi da gudanar da ayyukan jirgin lafiya.
“Hukumar ta NCAA ta amince da mummunan tasirin da wannan matakin da aka yanke zai haifarwa da fasinjojin jirgin da kuma jama’a masu balaguro tare da neman fahimtarsu, saboda amincin ayyukan jirgin yana ba da fifiko kan duk wasu la’akari.”
Idan za a iya tunawa, kamfanin jirgin saman na Aero mafi dadewa a Najeriya, shi ma ya dakatar da ayyukan jigilar fasinja har zuwa yau.
Jaridar Dimokuradiyya ta ruwaito cewa kamfanin, ya bayyana cewa an dakatar da ayyukansa ne saboda kalubalen da ke tattare da yanayin aiki a harkokin yau da kullum.