Rundunar sojin Najeriya ta kori wasu sojoji biyu da ke aiki da bataliya ta 241 da ke Nguru a jihar Yobe bayan samunsu da laifuka guda biyu.
A cewar Mukaddashin Kwamandan Bataliyar, Laftanal Kanal Ibrahim Abdullahi Osabo, an samu wadanda ake zargin da laifuka biyu; wato: rashin yin aikin soja; da kuma nuna son zuciya ga horon yin hidima, kamar yadda DAILYPOST ta bayyana.
Karanta kuma: Rundunar ‘Yan Sanda Ta Dakatar Da Jami’anta Guda Biyu
Wadanda ake zargin dai an rage musu mukamansu daga ma’aikatan kofur zuwa na sirri kafin sallamar su gaba daya.
Dimokuradiyya ta rawaito cewa, Idan ba a manta ba, ‘yan sanda a jihar Yobe sun kama Lance Kofur John Gabriel mai lamba N/A13/69/1522 da Lance Kofur Adamu Gideon N/A13/70/6552 da ke aiki da 241 Recce Battalion, da ke Nguru, a jihar Yobe bayan da ake zargin sun kashe wani shahararren Malamin addinin musulunci, Sheikh Goni Aisami cikin ruwan sanyi.
A wani labarin kuma: An Kori Wani Jami’in Ɗan Sanda Daga Aiki, Bayan Lakaɗawa Wani Na Jaki
Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta kori wani jami’inta, mai suna Liyomo Okoi bisa laifin yi wa wani mutum Lakadawa wani mutum na jaki.
An kama jami’in da aka kora a wani faifan bidiyo a ranar 31 ga Yuli, 2022 inda yake dukan wani mutum da adda.