By Abbas Yakubu Yaura
Rahotanni sun bayyana cewa rundunar ‘yan sandan ta kubutar da ma’aikatan jami’ar Abuja su shida da wasu ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su a ranar Talata tare da sada su da iyalansu.
Cikakkun bayanai na aikin ceton na da tsari amma kakakin rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, Josephine Adeh, ta tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ta fitar a safiyar yau.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa yadda aka yi garkuwa da wasu farfesoshi biyu, da ma’aikacin da bana ilimi ba, da kuma wasu mutane uku daga ma’aikatarsu.
‘Yan bindigar da yawansu ya haura 20 ance sun yi harbin a kan hanyarsu ta zuwa cikin harabar inda suka tafi da wadanda abin ya shafa.
Sai dai kuma Bayan sa’o’i 24, dayin garkuwa dasu sai masu garkuwar suka bukaci a biya su Naira miliyan 300 a matsayin kudin fansa.
Ba a iya tabbatar da ko an biya kudin fansa kafin a sako suba, kafin ‘yan sanda sun ceto wadanda lamarin ya rutsa da su.
Sai dai Adeh a cikin sanarwar tace, “Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja na son sanar da jama’a cewa an kubutar da duk wadanda aka yi garkuwa da su a Jami’ar Abuja tare da sada su da iyalansu ta hanyar hadin gwiwa da sauran jami’an tsaro.Karin bayani na nan tafe.”