An samu tashin hankali a wasu sassan jihar Sokoto a ranar Asabar din Nan, yayin da masu zanga-zangar suka bazama kan tituna domin sakin wadanda kama wasu da ake zargi da hannu a kisan wata daliba da ake zargin sun yi batanci.
Jaridar Dimokuradiyya ta ruwaito, yadda aka kashe Deborah Samuel, daliba mai mataki aji na 200level a Kwalejin Ilimi ta Shehu Shagari da ke Sokoto, bisa zarginta da aikata sabo.
Masu zanga-zangar sun yi amfani da kwalaye masu rubuce-rubuce kamar, “Ku saki ‘yan uwanmu Musulmi”, Musulmi ba ‘yan ta’adda ba ne, da dai sauransu.
Gabanin zanga-zangar dai an jibge jami’an tsaro a wurare masu muhimmanci da suka hada da fadar Sarkin Musulmi.
Da yake tsokaci a shafukan sada zumunta, wani Jefiter John, ya nemi mazauna yankin da su kasance a gida kuma su guji wuraren da masu zanga-zangar suke.
Wani mai amfani da shafukan sada zumunta ya nemi gwamnati da ta ayyana dokar hana fita domin samun zaman lafiya.
An fara samun matsala ne bayan da marigayiyar ta yi kalaman batanci a wani group na WhatsApp da abokan karatunta suke ciki.
“Jami’an tsaron kwalejin sun shiga tsakani ne ta hanyar garzaya da ita ofishinsu amma dalibai sun Fi karfinso, inda daga bisani suka kashe ta suka banka mata wuta,” wata majiya ta shaida wa Jaridar Daily Trust.
Gwamna Aminu Tambuwal ya gana da malaman addini a ranar Juma’a domin kwantar da tarzoma.