Daga Muhammad Muhammad
Wani rahoto da Jaridar Daily Correspondents ta labarto ya nuna cewa; shugaban kasa Muhammadu Buhari ya nemi hadin kan shugaban Rasha, Vladimir Putin domin ya taimaka masa musamman ta bangaren soji wajen kawo karshen ‘yan ta’addan Boko Haram arewa maso gabashin Nijeriya.
Rahoto daga kafar watsa labaran Rasha ta Kremlin’s RIA, wanda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya labarto, an bayyana cewa; shugaban kasa Buhari zai sanya hannu a wata yarjejeniya da kasar Rasha a birnin Sochi na kasar kafin karshen watan Oktoba.
Inda shi kuma Jakadan Nijeriya a Rasha, Stephen Ogbah ya ce yana fatan da hadin kan Rasha, Nijeriya ta gama da ‘yan ta’addan Boko Haram.
Inda ya ce; “ina da kwarin guiwa Nijeriya za ta kawo karshen Boko Haram idan har Rasha ta amince za ta tallafa wajen kawo karshen Boko Haram din musamman idan aka yi duba da kwarewarsu wajen yakar ‘yan ta’adda a Siriya.” In ji shi.
Ogbah ya ci gaba da cewa; Nijeriya tana sha’awar siyen tankokin yaki da jiragen yaki da sauran kayayyakin yaki na soji daga kasar Rasha, inda ya ce; tuni ma aka rubuta bukatar hakan.