Sarkin Kano na 14, Sanusi Lamido Sanusi, ya koka kan halin da al’ummar kasar ke ciki, yana mai cewa Najeriya ba za ta kasance inda take ba idan masu rike da mukaman gwamnati suka dauki aikinsu da muhimmanci.
Sanusi, wanda ya yi magana a Legas ranar Lahadin nan a wani wasan kwaikwayo na kan dabe mai taken “Sarki Sanusi: Gaskiyar Zamani”, “Emir Sunusi: Truth in time” ya bukaci ‘yan siyasa su kasance masu rikon amana ga jama’a.
Tsohon Sarkin Kano ya tuna yadda ya rubuta wasikar sirri ga tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan a daidai lokacin da yana gwamnan babban bankin Najeriya CBN ke bayyana damuwarsa kan tattalin arziki.
“Idan kowane shugaban kasa, kowane gwamna, kowane minista, kowane kwamishina ya dauki gaske, kasar nan ba za ta kasance inda take ba,” in ji shi.
“Idan mutane suna son zama ministoci, kwamishinoni, gwamnoni da shugaban kasa na tsawon shekaru takwas, kuma ba su gaya mana yadda suka inganta rayuwarmu ba, muna da matsala.”
KARANTA WANNAN: https://dimokuradiyya.com.ng/yan-bindiga-sun-yi-garkuwa-da-mutane-da-yawa-mutane-uku-sun-mutu-a-taraba/
Dimokuradiyya ta rawaito cewa, Ya bukaci ‘yan Najeriya da su karbi ragamar mulkin kasar, ya ce kasa mafi yawan al’umma a Afirka ba za ta ci gaba ba har sai an dauki hakikanin matakai.
Tsohon gwamnan na CBN ya kuma yi magana kan dalilin da ya sa ya saba sukar manufofin gwamnati, yana mai cewa abin da mutane da yawa ba su sani ba shi ne, ya shawarci jami’an a boye na tsawon watanni kafin ya fito fili.
Dangane da gwamnati mai ci, Sanusi ya ce ya gargadi gwamnatin tarayya kan illolin da ke tattare da manufofinta a shekarar 2015, musamman yadda za ta lalata tattalin arzikin kasar.
“Tare da gwamnati mai ci, na shafe tsawon shekarun 2015 da 2016 na yi magana da duk wanda ya kamata a sanar da su, tare da shaida musu cewa manufofin tattalin arzikin da suke bi za su lalata tattalin arzikin Najeriya.
“Sai da abin ya faskara na yi magana a bainar jama’a, kuma dole ne mu yi magana. Yanzu tambayar da kowa ke yi shine ya kamata sarki yayi magana? Amsar ita ce eh kuma ya danganta da abin da kuke magana akai,” inji shi.
A cewar Sanusi, ya yi aiki a matsayin Babban Jami’in Hatsari a Bankin United Bank for Africa, a Bankin First Bank, da kuma Gwamnan CBN; a matsayin Sarkin Kano na tsawon shekaru shida.
Ya bayyana cewa ba zai godewa Allah ba idan ya nuna nadama ko bakin cikinsa kan tsige shi a matsayin sarki duk da matsayinsa na rayuwa.
(Channels TV)