Hukumar Zaben Nijar Ta Kaddamar Da Shirin Yiwa ‘Yan Kasar Dake Kasashen Waje Rijista.
Sai dai a wasu kasashen kwamity dake da nauyin tafiyar da wadannan ayyuka na fuskanatar matsalloli, yayin da bangaren ‘yan adawa suka koka da irin yada hukumomin na Nijar suka mayar da su gefe.
A Cote D’ivoire, na’urorin da ake amfani da su domin yiwa jama’a rijista na fuskantar matsalloli kamar dai yada mai magana da sunan jam’iyyar adawa ta Lumana a kasar ta Cote D’Ivoire Elhaji Soumana Yakouba ya shaida.
A daya wajen Elh Soumana Yakouba ya yi amfani da wannan dama domin isar da ta’azziyarsa zuwa Shugaban Jam’iyyar Hama Amadou da Allah ya yiwa mahaifiyarsa rasuwa a Nijar.
Wasu bayanai na nuni da cewa yanzu haka wasu kasashe da suka hada da Faransa na kokarin shiga tsakani domin bai wa shugaban babbar jam’iyyar adawa a kasar Moden-Lumana Africa wato Hama Amadou damar komawa kasar, bayan da ya share dogon lokaci yana zaune a waje .
Yanayin siyasa a jamhuriyar Nijar na ci gaba da tayar da hankulan kungiyoyin fararen hula da wasu jam’iyyoyin siyasa.