Daga Aliyu muhammad, kaduna
JARIDAR DIMOKURADIYYA: Shekara daya kenan da wasu watanni ‘yan sanda suka je Rugarmu suka kore shanu na har 31 da tumaki 4″ Inji Wani Bafilatani mai Suna Ibrahim, dake garin kaban cikin karamar hukumar Igabi a jihar kaduna.
Ibrahim Yace sun zo ne da sunan suna neman ‘da na mai suna Habu, kuma basu sameshi ba sai suka koro shanu na, lokacin da ‘yan sanda suka koro shanun kuwa ‘ya’yana Abdulhamidu, da sulaiman, da matata Hafsatu, sun biyo wajen ‘yan sanda domin jin dalilin kama shanun suma sai aka kamasu aka tsare har saida aka karbi sama da dubu dari hudu kafin aka sake su.
Alhaji Ibrahim, ya kara da cewa “lokacin da wannan abin ya faru ina fama da ciwon ido anyimin aiki a asibiti shi yasa ban samu zuwa wajen ‘yan sanda ba sai na tura yara amma aka kamasu aka garkame” a cewar shi.
Alhaji Ibrahim Dan filani, shekarun sa 80 a duniya ya shaidawa manema labarai cewa sun je wajen ‘yan sanda har sun gaji domin a basu shanun su amma ‘yan sanda sai kudadensu kawai suke karba da sunan za’a basu dukiyarsu amma har yanzu babu labari.
Ya kara da cewa kasan mu Fulani, babu wani abu da muka sani idan ba shanu ba raba Bafillatani da shanu da “yan sanda suke yi shine yake kawo filani suna shiga harka ta banza”
“Yace shi shanunsa babu na sata a ciki kuma tun lokacin da ‘yan sanda suka koromasa shanu yau shekara daya kenan babu wani mutun da yazo ya nuna cewa shanun sa ne, kuma har kotu ta bada humarnin a kawo shanun Gabanta amma ‘yan sanda sunyi biris da maganar kotu.
Sai dai a ta bakin bangaren ‘yan sandan kuwa jami’in hulda da jama’a na ‘yan sanda a kaduna D S P Yakubu Sabo, yace yana kan binciken wannan Al’amari kuma yace zai bani hadin kai domin kara gano gaskiyar wannan batu.
A Karshe Alhaji Ibrahim, yayi kira ga shugaban ‘yan sanda na kasa da ya sanya baki a basu dukiyarsu domin kada yaransa su fada wata hanya ta banza.