Kwamishinan Yansandan Jihar Kano CP Muhammad Wakili,ya ce tun da aka kammala zabe zuwa yanzu sun kama ‘yan daba wadanda suke kurkuku fiye da 930.
Ya ce masu tu’ammali da miyagun kwayoyin sun suaya salo, “amma a yanzu haka muna binciken wani muhimmin batu.”
Ya ce yana nan daram dam kuma suna aikinsu yadda ya kamata.
“A baya an rika jin duriyata saboda lokacin zabe ne,” kamar yadda ya shaida wa wakilinmu Khalifa Dokaji a Kano ranar Laraba.
A wata hira da yayi da BBC yace “Ana gwagwarmayar neman zabe akwai abubuwa da dama wadanda na tsaro ne wanda yake dauke hankalin jama’a.
“Saboda haka yana bukatar a ji tabbacin cewa za a yi lafiya a gama lafiya…wanda yake duk yanzu babu su,” in ji shi.
Daga nan ya ce yana nan lafiya lau kuma yana aikinsa yadda ya kamata.