By Abbas Yakubu Yaura
Rahotannin sun bayyana cewa Dalibai uku ne suka jikkata tare da lalata dukiyoyi a wata gobara data tashi a dakin kwanan dalibai mata na Murtala dake Jami’ar Maiduguri a ranar Asabar, wanda shi ne karo na biyu da ake samun irin wannan lamari cikin wata guda.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa Wutar wadda ake zargin ta taso ne daga murhu na dafa abinci,inda tuni hukumar kashe gobara ta jami’ar ta samu nasar kashe ta.
Da yake tsokaci kan lamarin, Daraktan hulda da jama’a na jami’ar, Farfesa Danjuma Gambo, yace binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa fashewar tukunyar kananzir ce ta haddasa lamarin, kuma matan uku da lamarin ya rutsa dasu suna kwance a asibiti.
Gambo, wanda ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici, yace hukumar jami’ar na daukar matakan kara tabbatar da karin ka’idojin kashe gobara a gidajen kwanan dalibai.
Comments 1