• Sai da daibin ya aike da sakon janhankali zuwa ga shugaba makarantar kafin ya yanke hukuncin.
• Dalibin zai kai karan makarantar ne sakamakon korar shi da ta yi.
•Jami’in hulda da jama’a na jami’ar ya ki cewa komai dangane da lamari.
Wani dalibi dake aji 5 a jami’ar jihar Akwa Ibom Ekpo Iniobong, ya yanke shawaran kai karar jami’ar, biyo bayan dakatar da shi, da koran shi da jami’ar ta yi
Jaridar PUNCH ta ruwaito cewa, tun da farko a watan satunbar shekarar 2020 an dakatar da dalibin ne, dake ajin karshe a sashin nazarin injiniyancin aikin gona, bisa zargin wani rubutu da ya wallafa a shafin shi na Facebook, na nuna adawa da gwamnan jihar Emmanuel Udon.
Sai dai tun a ranar 18 ga watan Yunin shekarar nan, dalibin ta hannun lauyan shi Inibehe Effiong, ya tura da wani sakon janhankali zuwa shugaban jami’ar Farfesa Essien, inda ya bukaci da ya yi gaggawar janye hukuncin da aka dauka kan dalibin.
A cewar lauyan, matakin da jami’ar ta dauka kan dalibin ya saba wa sashin 36 na gyararriyar kundun dokar kasa Nijeriya, na shekarar 1999, da kuma doka ta 7 na tauye hakkokin dan Adam.
KARANTA WANNAN LABARIN: Wani mutun ya yi wa yar shekara 60 fyade
Sai dai ko da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na jami’ar Akeninyene Ibanga, domin ya yi karin haske kan lamarin.
Ya ce, “Yanzu ba a shirye nake ba, na yi magana kan wannan batu” inji shi.