Gwamnan jihar Kwara, ta ce rike da ayyukan al’umma da Saraki ya yi ya ki yi musu yana daya daga cikin dalilan da ya sanya suka ki karbar kyautar da Dr Bukola Saraki ya yiwa wadansu makarantun gwamnati.
Sakataren watsa labaran ma’aikatar ilimi, Yakub Aliagan shi ne ya bayyana hakan a ranar Litinin, inda ya ce ma’aikatar tun farko ma ba su da masaniya akan wannan kyautar. Ma’aikatar ta kara da cewa; tun farko abin da ya kamata Saraki ya yi shi ne ya aikata kayayyakin taimakon ga ma’aikatar ilimin, sannan su duba nagartar kayayyakin koyon ilimin, daga nan sai a amince masa da ya je ya raba. Sun kara da cewa abin da Saraki ya sabawa ka’ida wanda kuma bin ka’idar nan ne kawai zai bunkasa hukumar a cewar su.
Sun kara da cewa ba ya ga haka, bai dace wani ya raba kayayyakin karatu dauke da hotonsa ba, ko wani abu daban da kawai shi ya kebanta. Inda suka ce; kayayyakin ma kayayyakin da gwamnatin tarayya ta dauki nauyi ya raba a yankinsa.