A ranar Laraba Fadar shugaban kasa, ta bayyana cewa, Shugaba Muhamamdu Buhari ya ba da umarnin cire wasu kudade kwanaki kalilan kafin mika mulki ga shugaba mai jiran Gado Bola Tinubu, saboda gwamnatin na bukatar kudi domin biyan wasu basussuka. Kamar yadda Channels TV ta ruwaito.
Mataimaki na mussamman ga shugaban kan Kafafen yaɗa labarai, Femi Adesina ne ya bayyana hakan yayin da yake jawabi a cikin shirin siyasa na gidan Telebijin na Channels mai suna Politics Today” yayin da ake karin haske akan ayyukan da gwamnatin shugaba Buhari ta aiwatar a cikin shekaru 8.
KARANTA WANNAN LABARIN: Bankuna Yanzu Zasu Iya Bayar Da Katin Ƙasa — FG
A ranar Laraba da ta gabata ne shugaba Buhari ya aike wa majalisar Dattijai takar da neman amincewa kan biyan bashin wasu kuɗaɗe da suka kai Dalar Amurka Miliyan dari biyar da sittin da shida da ɗigo bakwai (566.67) da wasu Yuro dubu Tamanin da takwas da dari biyar da ashirin da shida, da kuma wani bashin da ya kai Naira biliyan 226.
Gidàn Telebijin na Channels ya rawaito cewa gwamnatin Tarraya ce keda mallakin kuɗaɗen.
Shugaban Majalisar Dattijai ta ƙasa , Ahmed Lawan ne ya karanta wasikar shugaban kasan yayin zaman majalisar da ka gudanar a ranar Laraba.
Wannan na zuwa ne bayan shafe wata huɗu da aka bada rahotonni makaman ta wannan guda 648 daga ɓangaren shugaban ƙasa da kuma wasu Ma’aakatun gwamamnati.
To sai dai Shugaba Buhari ya kasa rusa majalisar zartarwa ta ƙasa a zaman ƙarshen na Majlisar da gudana a ranar Assabar, koda yake Adesina yace babu wata doka da tace dole ne shugaban ƙasa ya rusa majalisar zartarwa sa a zaman ƙarshe na majalisar.
Mataimaki ga Shugaban kasar yace gwamamnatin shugaba Buhari bata yaƙar masu faɗin ra’ayinsu , inda ya ƙara da cewa suna karɓa tare da Mutun ta kowanne irin ra’ayi.
Yace masu suka suna da incin akan ra’ayoyin su , Adesina ya bayyana cewa akwai bayyanai da a ka wallafa wadanda ke nuni da cewa gwamnatin tayi aiki tuƙuru kuma ta cimma nasarori da dama.
A wani cigaban kuma, Aikin Hajji: Alhazan Najeriya Zasu Ci Abincin Gida A Saudiyya — NAHCON
Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta tabbatar wa alhazan Najeriya cewa za a ciyar da su abinci na gida yayin gudanar da aikin hajji a kasar Saudiyya. Kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.
Da yake jawabi yayin kaddamar da jigilar maniyyatan Najeriya a ranar Alhamis, Shugaban Hukumar NAHCON, Zikrullah Hassan ya ce, mahajjata ka iya samun amincin da suke so a yayin aikin.