Duk da cire musu dokar hana fita a zamanin mulkin ‘YarAdua, Sadiq Abacha ya koka game da irin tsangwamar da suke fuskanta a wajen hukumomin kasar nan a duk lokacin da zasu fita ko shigo cikin kasar nan.
“Mun je wajen jami’an tsaro kuma sun bamu takardar shaidar wucewa amma bayan dana dawo daga Dubai sai da aka tsareni ana min tambayoyin wulakanci”.
Sadiq ya bayyana haka ne a yayin da yake tattaunawa da sashin Hausa na BBC a yau Laraba.
https://dimokuradiyya.com.ng/amurka-ta-maido-wa-najeriya-dala-miliyan-311-na-abacha/
Da aka masa tambaya game da irin rahotannin da suke bayanna kudaden da mahaifinsu ya kai kasashen ketare, Sadiq ya bayyana damuwarsa game da rahotannin.
“Watakila akwai dalilin da yasa aka kai ajiye kudaden a can, sannan akwai siyasa a lamarin, amma gaskiya bana murna da yadda lamarin yake faruwa”.
Sadiq ya kara da cewa iyalan tsohon shugaban kasa Babangida ne kadai suke kula da zumuncinsu, amma shugaban kasa Muhammadu Buhari ya watsar dasu babu wata kulawa da suke samu daga wajensa.
“Duk da tsohon sakataren gwamnatin tarayya Yayale Ahmed, ya taimaka wajen cire mana dokar fita waje, amma babu abinda ya sauya ko a lokacin dokar kullen nan da ake ciki dana dawo daga Dubai sai da aka tsareni domin yi min tambayoyi”.