A watan Oktobar mai zuwa ne hukumar zabe mai zaman kanta a jihar Bauchi ta shirya tsaf domin gudanar da zaben shugabannin kananan hukumomi 20 na fadin jihar Bauchi.
Najib Sani, sanannen dan jarida a jihar ya nuna sha’awarsa ta tsayawa takara domin neman kujerar shugaban karamar hukumar na Bauchi.
Najib Sani dai shi ne wakilin Jaridar Blueprint a jihar Bauchi kuma shi ne Sakataren kudi na kungiyar ‘yan jarida reshen jihar (NUJ) ya shelanta muradinsa ne a wata kwafin sanarwar manema labaru da ya fitar a ranar Talatar da ta gabata.
Najib ya shaida cewa zai nemi takarar ne a karkashin jam’iyyar APC wanda kuma zai gabatar da fom din da ya cika don neman tsayawa takarar a ranar Laraba domin tsunduma harkar neman kujerar gadan-gadan na jihar.
A cewarsa, mutane da yawa da suke takara a ofisoshin kananan hukumomi a kasar nan ba su da wayewar mulki sosai kuma ba su san abin da jagoranci ya kunsa ba tare da jaddada cewa kananan hukumomi muhimmai ne na gwamnatocin da ke bukatar mutane masu nagarta da kwarewa tare da sanin dabarun yin jagoranci.
Ya yaba wa gwamnan Bala Muhammad a bisa tunaninsa na yin zaben kananan hukumomi a maimakon ya dage wajen nada shugabannin riko a kananan hukumomin, daga nan sai ya hori gwamnan da ka da ya nace wajen mara wa jam’iyyarsa ta PDP baya, yana mai cewa yin hakan shi ne zai wanzar da zabe mai nagarta kuma cikin adalci.
“Ina mai farin cikin sanar da ku cewa na yanki fom din tsayawa takara don fitowa a dama da ni a zaben Shugabannin kananan hukumomi da ke tafe a watan Oktoba. Ina neman kujerar shugaban karamar hukumar Bauchi ne. Na yi imani yanzu ne lokacin da ya dace matasa su rungumi mutuncinsu da kimarsu a hannunsu.” a cewar shi.
Ya shaida cewar yana son jam’iyyar APC ta ba shi tutarta domin ya shiga fagen dagar nema mata nasara a zaben da ke tafe don haka ne ya nemi goyon baya ga wadanda suka dace domin ya kai ga cimma nasara.