Wani dan sanda wanda aka bayyana sunansa a matsayin Sajan Taiwo Orisadare ana zarginsa da dabawa wasu mutum 9 wuka a wani sanannan gidan casu da ke garin Akure, a jihar Ondo. Rikici ne ya barke a gidan casun da daddare. Wanda a karshe ya yi sanadiyyar dan sandan ya dabawa mutum tara wuka.
Gidan casun wanda ya kasance yana unguwar Alagbaka GRA a garin Akure. Rahotanni sun tabbatar da cewa; dan sanda wanda ke karkashin rundunar ‘yan sanda da ke yankin Akure shi ne ya fara tayar da rikici a gidan casun.
A cewar wani mutum wanda ya shaida faruwar hakan, ya bayyana cewa dan sanda haka kawai ya fara dukan mutanen da suke cikin gidan casun.
Wani daga cikin mutanen da suka shaida faruwar hakan wanda ya bayyana mana yadda abin ya faru ya ce; haka siddan a bayyane Sajan Orisadare wanda barasa ta bugar da shi, ya aikata wannan aika-aika.
Bayanai sun nuna cewa; a lokacin da yake wannan mummunan aiki ya ki jin maganar kowa a yayin da aka fada masa ya dau komai a hankali. “Kawai a lokacin daya kawai abun ya kara rikicewa inda ya fara dabawa duk wani mutumin da ya samu wuka. Ya dabbawa akalla mutane 8 wuka kafin aka sha karfinsa” In ji ganau.
A halin yanzu wasu daga cikin mutanen da dan sandan ya dabawa wuka suna asibiti daba- daban da ke fadin garin. Kakakin rundunar ‘yan sanda na jahar, Fem Joseph, ya bayyana cewa dan sanda tare da wadanda aka dabawa wukan sun kasance cewa rikici ne ya barke a tsakaninsu.