A yau asabar aka rantsar da sabon Shugaban kasar Salvador Nayib Bukele mai shekara 38 da ya yi nasara a zagayen farko tare da lashen zaben Shugabancin kasar da kuri’u kashi 53 cikin dari da aka kada a zaben watan Fabrairu. Kasar na daga cikin kasashen da cin hanci da rashawa ya yiwa katutu, Shugabannin kasashen da suka taba rike muakamin shugabanci na fuskantar tuhuma biyo bayan samun su da laifin azurta kan su ta hanyar da ba ta dace ba. A wannan bikin da ya gudana babban birnin kasar San Salvador, dubban ‘yan kasar suka fito domin sake jaddada goyan bayan su yayin da manazarta ke bayyana cewa kalubalen dake gaban sabon Shugaban kasar za su hada da yaki da cin hanci da karbar rashawa daga jami’an gwamnati.