Davido ya bada tallafin karatu ga wani Ɗalibi a Ghana
Fitaccen Mawaƙi a Najeriya Davido ya bada tallafin karatu ta shekara biyar ga wani Ɗalibi ɗan Asalin Ƙasar Ghana, wanda bai samu damar cigaba da karatun sa.
KARANTA WANNAN LABARIN: Rundunar ‘Yan Sanda Ta Tabbatar Da Sace Matafiya Bakwai A Jihar Kogi
A cikin wani saƙo daya watsu a kafar Twita, wani Ɗalibi da ake kira da Morro Suleyman, daya ci sakamako mai kyau na A1 bayan ya zauna Jarabawa Ƙasashen Yammacin Afirka (WAEC) a shekarar 2021, shima bai samu damar zuwa Jami’a a dalilin matsalar kuɗi.
Mawaƙin wanda yayi kokari wajen gano yaron, ya sanar da cewa ya ga Morro Suleyma, Kuma ya bashi tallafin karatu na shekara huɗu zuwa biyar a Jami’ar Adeleke da wurin kwana da Alawus-Alawus.
David ya rubuta “mun tuntubi Suleyman wanda yake zaune a Ghana, tallafin karatu na shekara huɗu zuwa biyar a Jami’ar Adeleke, da wurin kwana, da Alawus-Alawus.
Comments 1