Wani ganau mai suna Adama Mallum, a ranar Alhamis ne yake shaida wa babbar kotun a cikin birnin tarayya FCT cewar ya ji Sanata Dino Melaye da ke wakiltar Kogi ta Yamma yana shan alwashin cewar zai kashe kansa da kansa domin ya jefa ‘yan sanda cikin matsala. Mista Mallum, wanda dan sanda ne mai mukamin Insifekta kuma Direba ne, ya ce ya jiwo Melaye na wannan ikirarin ne a lokacin da ke kokarin arcewa a lokacin da ke tsare a hanun ‘yan sanda. Ya shaigar da wannan zargin nasa ne domin tabbatar wa a ci gaba da shari’ar da ke kan Melaye na kokarin kisan kai a lokacin da ya yi yunkurin arcewa daga magarkamar ‘yan sanda hadi da lalata wa ‘yan sanda kayyakinsu. Mista Melaye yana fuskantar kararraki ne har guda shida da suka hada da kokarin kisan kai, kokarin arcewa daga hanun ‘yan sanda, hadi da lalata kayyakin ‘yan sanda. Shaidar ya shaida wa kotun cewar a wata ranar 24 ga Afirulun 2018 a lokacin da suke bakin aiki, wani dan sanda mai suna Amos Boka, mai mukamin ASP ya shaida masa za su tafi don zuwa Lakoja don yin rakiya ga tawagar Melaye da wasu jami’an ‘yan sanda zuwa Lakoja. “Muna tafiya wajajen karfe biyu na rana a daidai shataletalen Area I, wata mota fara kirar Toyota Hilud ta rufe ni, nan take na motsa ni ma, motar ta balle min mirona. “Na jiyo Sanata yana ihu ga jami’an ‘yan sanda. Sannan sai na ji sautin ya farfasa kilashin motar. “Nan da nan, sai Sanata Melaye ya yi tsalle ya fita daga motar, yana ihun cewar ba zai je Lakoja ba,” Kamar yadda ya shaida. Mai bayar da shaidar ya kuma yi zargin cewar Melaye wanda ke rike da wani abu mai kaifi a hanunsa inda ke cewa, “Sai na kashe kaina na jefa ‘yan sanda cikin mawuyacin hali,” “A wannan lokacin jami’an ‘yan sanda sun roke shi da ya koma cikin motar amma ya bijire wa hakan,” “Har ila yau, a lokacin da jama’a suka fara taruwa a wurin Area I, an umurce ni da na sanya motar a baya domin mu sake komawa ofis,” Mista Mallum ya yi zargin cewar wata farar babban mota ta rufe motar da yake tukawa. Lauyan kariya, Aled Izinyon (SAN) ya roki kotun da cewar a je wuraren adana motocin domin shi wanda ke wannan ikirarin ko zai iya gano wannan motar da yake magana a kanta. Mai shari’a Silbanus Oriji, ya dage ci gaba da sauraron karar zuwa ranar 27 ga watan Mayu domin ci gaba.