Didier Drogba mai shekaru 42 da haihuwa a duniya, ya gabatar da shaidar takardun tsayawa takara da ya cike a hukumance tare da rakiyar ɗaruruwan magoya baya da suka yi jerin gwano, inda ya kasance mutum na 4 da ke takarar shugabancin hukumar ta kwallon kafa ta ƙasar Ivory Cost.
To sai dai babu tabbacin cewa tsohon gwarzon ɗan kwallon na Afirka zai kasance a cikin ‘yan takara na ƙarshe na zaɓen da za’a gudanar a ranar 5 ga watan Satumba shekarar nan.
Ko baya ga sharadin samun goyon bayan kungiyoyi 3 daga cikin 14 da ke fafata gasar Ligue 1 da kuma kungiyoyi 2 da ke buga kananan gasanni, wajibi ne kuma Drogba ya samu amincewa da goyon bayan ɗaya daga cikin rukunnan ƙungiyoyi na musamman, kamar masu horar da ‘yan wasa, likitoci, gungun ‘yan wasa na da da na yanzu da kuma na alkalan wasa.
Waɗannan rukunnan ba su kai ga fitowa fili suka bayyana ɗan takarar da za su goyi baya ba, haka kuma wata hukumar zaɓe ce za ta soma tantance ‘yan takarar kafin su iya tsayawa takara a zaɓen hukumar.
Ana sa ran sakamakon tantance ‘yan takarar na ƙarshe zai fito nan da kwanaki biyar, in ji mai magana da yawun hukumar kwallon kafar kasar.
Drogba ya bugawa kasarsa ta Ivor Cost wasa a gasanni 3 na cin kofin duniya, kuma sau 2 yana bugawa kasar wasa tana lashe gasar cin kofin nahiyar Afirka.
Tauraruwarsa ta haska sosai har ya yi suna a zamansa ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Chelsea dake ƙasar Ingila, inda ya lashe gasannin Premier da Zakarun Turai.