Kwamitin fadar shugaban kasa mai yaki da cutar Korona a Nijeriya ta bakin shugabanta Boss Mustapha a yau Litinin ya sanar da tsawaita dokar hana zirga-zirga a jihar Kano da karin makwanni biyu.
Da yake jawabi ga manema labarai Sakataren gwamnatin tarayya Boss Mustapha ya ce har wa yau dokar saka tazara a tsakanin al’umma da ma ta zirga-zirga tsakanin jihoji su ma duk an kara musu makwanni biyu.
Boss Mustapha ya kara da cewar wannan yaki da ake da cutar Korona ba abu ne da zai kare rana daya ba, a sabili da haka duk jihar da aka samu karuwar cutar za a iya saka mata wannan doka da Kano ke ciki.
Jihar Kano dai na zama ta biyu a fadin Nijeriya da alkalumman wadanda ke dauke da cukar suka haura mutum dari takwas kana sama da mutum 35 su ka rigamu gidan gaskiya.
Sai dai duk da wannan doka ta gwamnatin tarayya ta sanya a Kano, gwamnan Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya bada damar fita a yi sallar Juma’a da Idi, tare da bada damar fita a ranekun Litinin, Laraba da Juma’a.