Tsohon shugaban ƙasar Najeriya Chif Olusegun AremuOAremu ya ce mutuwar Sanata Buruji Kashamu izna ce ga kowa domin duk da irin dabarun mamacin ya kasa tsere wa mutuwa.
Obasanjo a sakon ta’aziyyar Buruji ya ce duk da dabarun marigayin na tsere wa shari’ar laifuffukan da ake zarginsa da aikatawa a ciki da wajen Najeriya, hakan bai sa ya iya tsere wa mutuwa ba.
“Na samu mummunan labari na mutuwar Sanata Buruji Kashamu wanda mutum ne muhimmi a Jihar Ogun; ina mai mika ta’aziyyata da ta iyalina a kan wannan babban rashi.
https://dimokuradiyya.com.ng/korona-sanata-buruji-ya-rasu-sakamakon-cutar-korona/
“Rayuwa da tarihin marigayin izna ce gare mu baki daya, domin Sanata Buruji Kashamu a lokacin rayuwarsa ya yi ta guje wa fuskantar shari’ar laifukan da ake tuhumarsa da su a ciki da wajen ƙasar nan.
“Amma da mutuwa ta zo masa babu dabarar likitanci ko ta siyasa ko al’ada da ta hana ta ɗauke shi a daidai lokacin da Mahaliccinsa Ya yi wa’adinsa ya cika.
Daga ƙarshen tsohon shugaban ƙasar ya yiwa mamacin fatan alheri da kuma jajantawa iyalansa.