Hukumar ‘yan sanda sun gano wani matashi mai shekaru 35 da iyayensa suka kulle shi a ɗaki na tsawon shekara 15 ba tare da yana samun isasshiyar iska ba.
‘Yan sandan da suka kuɓutar da Ibrahim Lawal a unguwar Sheka, sun garzaya da shi zuwa Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano kamar yadda wakilinmu ya bayyana mana.
Wakilimu ya ce mahaifin matashin, Malam Lawal Sheka wanda aka ce limamin wani masallacin Juma’a ne ya tsere tun bayan samun labarin ‘yan sanda sun kuɓutar da ɗan nasa.
Zuwa yanzu mahaifin matashin da ake zargi da kulle dansa tsawon lokacin bai ce uffan game da dalilinsa na yin hakan ba.
Jami’an rundunar’ yan sandan da ke aiki a shiyar ƙaramar hukumar Kumbotso a ƙarƙashin jagorancin Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar Kano, Habu Ahmad Sani da kuma Baturen ‘Yan Sandan yankin ne suka kai wa matashin ɗauki.
Hakan na zuwa ne kwana biyu bayan ‘yan sanda a jihar ta Kano sun gano wani matashi Ahmad Aminu mai shekara 32 da iyayensa suka kulle a ɗaki na shekara bakwai.
Ana zargin mahaifin matashin da kishiyar mahaifiyarsa da kulle shi saboda zargin yana shan ƙwaya.