Waɗansuu ƙananan yara ’yan ƙasa da shekara 20 su huɗu sun bayyana yadda suka haɗa wani gungun garkuwa da mutane inda suka sace wani yaro ɗan shekara shida suka nemi fansar Naira miliyan biyu da rabi.
Lamarin yaran ya jefa jama’a a cikin damuwa ƙwarai da gaske, ganin ba wanda ya kai shekara 20 a cikin yaran.
Yaran da suka haɗa da wani wani saurayi mai shekara 19 da ke zaune a Unguwar Borno kuma ɗalibi a Kwalejin Shari’a ta AD Rufa’i da ke Misau.
Akwai kuma wani mai shekara 18 shi ma da ke Unguwar Borno da abokinsu mai shekara 19 da ke Unguwar Madina, sai na ƙarshen mai shekara da ke Unguwar Borno.
Wakilinmu ya ce matasan sun amince da aikata laifin a lokacin da rundunar ’yan sandan jihar Bauchi ta gabatar da su ga ‘yan jarida a farkon wannan mako.
Ɗaya daga cikin samarin ya ce sun saci yaron ne domin su samu kuɗin da za su buɗe harkokin kasuwanci ko sana’a, inda ya ce shi burinsa ya buɗe shagon ɗinki.
Su ma abokansa uku sun ce burinsu shi ne idan suka samu kuɗin za su fara yin sana’o’i ne.
Abdulgafar ya ce ya iya ɗinki kuma ya roƙi mahaifinsa ya ba shi kuɗi ko rance ne, amma ya ce ba shi da su.
Saboda haka ne ya shawarci abokansa kan su sace ɗan makwanbicinsu ko za su samu kuɗin don su yi jari.
Ya ce, “Mun shirya komai har da inda za mu ajiye yaron,” kuma wanda suka ajiye yaron a gidansu ya yi karya ga mahaifiyarsa cewa yaron, ƙanin abokinsa ne da aka kwantar da mahaifiyarsa a asibiti.
Amma washegari sai mahaifiyar da hankalinta bai kwanta ba ta sanar da maƙwabta.
Ya ce ba su samu kuɗin ba, domin bayan sun daidaita a kan Naira miliyan ɗaya, a ranar da suka yi za su karɓi kuɗin ne aka kama su.
Ya ce sun yi dana sanin aikata wannan mugun aiki kuma idan har aka sake ba su dama za su yi rayuwa mai kyau.