By Ishaq Dabai
Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen Afirka ta Yamma ECOWAS a ranar Alhamis ta sanya takunkumi kan gwamnatin mulkin sojin kasar Guinea da wadanda ke sassauta sauyin mulkin Mali bayan juyin mulkin da akayi.
Takunkumin shine martani mafi tsauri na kungiyar har yanzu ga rundunonin sojojin da sukayi juyin mulkin.
An amince da wannan matakin a wani taron gaggawa da kungiyra ECOWAS ta gudanar a Accra don mayar da martani ga juyin mulkin da aka yi a kasar Guinea a makon da ya gabata, kuma ana ganin ci gaban da ake samu zuwa tsarin mulkin Mali bayan juyin mulkin bara.
Shugabannin yankin sun yanke shawarar da katar da kadarorin kuɗaɗen tare da sanya takunkumin tafiye tafiye ga membobin mulkin sojan Guinea da danginsu, tare da dagewa kan sai an saki shugaba Alpha Conde da ɗan gajeren sauyi.
Shugaban kwamitin ECOWAS Jean Claude Kassi Brou ya ce “cikin watanni shida ya kamata a gudanar da zabe.”Kungiyar ta kuma kara matsin lamba ga gwamnatin rikon kwaryar ta Mali, inda ta bukaci su tsaya kan yarjejeniyar shirya zabe a watan Fabrairu na 2022 tare da gabatar da taswirar zabe nan da wata mai zuwa, a cewar sanarwar bayan taron.
Duk wanda a Mali ya hana shirye shiryen gudanar da zabe yana iya fuskantar takunkumi daidai da wanda aka sanya a Kasar Guinea, in ji ta.
Shugabannin da suka halarci taron sun yaba da wannan tsayin daka, inda suka ammance da Tsakiyar Afirka sun ga juyin mulki sau hudu tun bara tashin hankalin siyasa wanda ya kara nuna damuwa game da koma baya ga mulkin soja a yankin da ke da arzikin albarkatu amma talauci.